19 Afirilu 2016 - 15:07
Bam Ya Kashe Mutane 28 A Kabul

Rahotanni daga Afganistan na cewa akalla mutane 28 ne suka rasa rayukan su a harin da kungiyar Taliban ta dauki alhakin kaiwa a birnin Kaboul.

Harin da aka kai da wata mota a wannan safiyar yayi kuma jikkata mutune sama da 200.

Wasu rahotanni na daban sun ce an yi ta harbe-harbe daga bisanin harin, lamarin da yayi sanadin mutuwar fararen hula da dama da kuma jami'an tsaro.

An dai kai hari ne a harabar ma'aikatar tsaron kasar dake Kaboul.

Tuni dai shugaban kasar Ashraf Ghani ya fitar da sanarwar yin allawadai da wannan harin.288